Wednesday, June 18, 2008

FALALAR AIKIN HAJJI

FALALAR AIKIN HAJJI

Allah ya kwadaitar damu yin aikin hajji kuma ya bayyana d'umbin ladar da za'a samu a sakamakon hakan hadisan dasuke zuwa zasu bayyana haka:

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : ( Duk wanda yayi Hajji, be yi rafasu ba - wato beyi Jima'i a cikinsa ba- kuma beyi fasikanci ba –wato sab'on Allah- ze koma mara laifi kamar randa mahaifiyarsa ta haifeshi ) Bukhari da Muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : (Yin aikin Umurah zuwa Umurah ana kankare zunubbai dake tsakaninsu, shiko aikin Hajji karbabbe baya da sakamako se Aljanna.) Bukhari da muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : yayinda aka tambayeshi gameda mafificin ayyuka se yace " Imani da Allah da manzansa" akace seme kuma? Yace "se jihadi dan daukaka kalmar Allah" akace se me kuma? Yace" se aikin Hajji karbabbe". Bukhari da Muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam………………..

SHARUDDAN WAJABCIN HAJJI

Seda sharudda masu zuwa hajji yake zama wajibi:

1. Musulunci

2. Balaga

3. Hankali: wato yakasance me hankali domin Hajji baya wajaba akan mahaukaci.

4. Y'anci: wato yazama d'a,domin hajji baya zama wajibi akan bawa. Dalilan wadannan sun gabata a cikin rukunin Azumi.

5. Samun iko: kamar yadda Allah madaukakin Sarki yace ( kuma lallai Allah ya wajabta wa mutane yin Hajjin dakinsa ga wanda yasami iko….) Sur. al'imrana -97.

No comments: