Wednesday, June 18, 2008
FALALAR AIKIN HAJJI
FALALAR AIKIN HAJJI
Allah ya kwadaitar damu yin aikin hajji kuma ya bayyana d'umbin ladar da za'a samu a sakamakon hakan hadisan dasuke zuwa zasu bayyana haka:
Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : ( Duk wanda yayi Hajji, be yi rafasu ba - wato beyi Jima'i a cikinsa ba- kuma beyi fasikanci ba –wato sab'on Allah- ze koma mara laifi kamar randa mahaifiyarsa ta haifeshi ) Bukhari da Muslim.
Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : (Yin aikin Umurah zuwa Umurah ana kankare zunubbai dake tsakaninsu, shiko aikin Hajji karbabbe baya da sakamako se Aljanna.) Bukhari da muslim.
Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : yayinda aka tambayeshi gameda mafificin ayyuka se yace " Imani da Allah da manzansa" akace seme kuma? Yace "se jihadi dan daukaka
Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam………………..
SHARUDDAN WAJABCIN HAJJI
Seda sharudda masu zuwa hajji yake zama wajibi:
1. Musulunci
2. Balaga
3. Hankali: wato yakasance me hankali domin Hajji baya wajaba akan mahaukaci.
4. Y'anci: wato yazama d'a,domin hajji baya zama wajibi akan bawa. Dalilan wadannan sun gabata a cikin rukunin Azumi.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment